Saturday, March 26, 2022

SAMANIYA


Domin Murtala Uba

 

Can take bisa kawunanmu
Sai mun xaga kai da idanuwanmu
Ta yi qoli, ba mai iya sa gannanmu
Su hango ina ta kare daga lungunnanmu

Ita ce xauke da iska don mu shaqa
Daga gareta rana ke haska mu ba mushaqqa
Hadari da girgije na nan kowace kiqa
Halitta ce ta Mafi zalaqa

Sama, ba wasa aka yi ta
Ta wuce duk tunani na fahimta
Babu sanin iyakacinta
Sai Allahu da yake halinqinta

Ga duniyoyi ko’ina an aje su
Ga taurari gari-gari aggaresu
Kai, ko yula da mashi Ya saka su
Kowane na bin umarnin Ubangijinsu

 

Allahu Mai halitta ba irinsa
Ikonsa ya fi tunanin halittarsa
Qarfinsa ya wuce ai musunsa
Huwallazi wanda babu irinSa.

  • Locations of visitors to this page

Blog Archive

About Me

My photo
Kano, Kano, Nigeria
Dr. Yusuf M. Adamu, Fulbright Fellow, member, Nigerian Academy of Letters and Fellow of the Association of Nigerian Authors is a Professor of Medical Geography at the Bayero University Kano. He is a bilingual writer, a poet, and writes for children. He is interested in photography and run a photo blog (www.hausa.aminus3.com) All the blogs he run are largely for his hobbies and not his academic interests. Hope you enjoy the blogs.